Header Ads

An kai harin da ya hallaka mutum 42 a wasu kauyukan Zamfara




Latsa alamar lasifikar da ke sama don sauraron abund a Sarkin Shanun Shinkafin ya shaida wa BBC:
Wasu da ake zargi 'yan bindiga ne sun kai hari a wasu kauyuka da ke karamar hukumar Shinkafi inda mazauna yankin suka ce ''an kashe a kalla mutum 42.''
Maharan dai sun kai harin ne a kauyukan da suka hada da Kurya da Kursasa da wasu kauyuka da ke yankin inda suka yi ta harbin mai uwa da wabi.
A hirar da BBC ta yi da Dakta Suleiman Shuaibu Shinkafi wanda shine Sarkin Shanun Shinkafi, ya bayyana cewa wannan ba sabon abu ba ne irin wannan harin da ake kai masu a wannan yanki.

No comments

Powered by Blogger.